1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An girka sabuwar gwamnatin rikon kwarya a Falasdinu

February 6, 2012

Kungiyoyin Hamas da Fatah masu hammaya a Falasdinu sun amince su kafa gwamnatin rikon kwarya karkashin jagorancin shugaba Mamud Abbas

https://p.dw.com/p/13xvO
GettyImages 137185648. LONDON - JANUARY 16: Britain's Prime Minister David Cameron (not pictured) speaks with Palestinian Authority President Mahmoud Abbas, prior to their meeting at his official residence at 10 Downing Street on January 16, 2012 in central London, England. Israel's ongoing building on land the Palestinians hope will form part of a future state was an issue discussed by the two leaders. Furhermore, Cameron stated that time was "running out for the two-state solution unless we can push forwards now." (Photo by Lefteris Pitarakis - WPA Pool/Getty Images)
Shuagab Mahmud Abbas na FalasdinuHoto: Getty Images

Kungiyoyin da ke hammaya a Falasdinu, wato Fatah da Hamas sun amince su girka gwamnatin rikon kwarya, karkashin jagorancin shugaba Mahmud Abbas. Shugaban zai jagorancin gwamnatocin da ke yamma da gabar tekun Jordan da kuma zirin Gaza kamar yadda wani babban jami'i wanda ya wakilci gwamnatin ya bayyana, bayan tattaunawar da kungiyoyin suka gudanar a Katar. Ana sa ran a 'yan watanni masu zuwa kungiyoyin na Fatah da Hamas zasu kuma sake amincewa da jadawalin gudanar da zaben Majalisar dokoki da na shugaban kasa. Tun a bara Kungiyoyin biyu suka rattaba hannu kan wata yarjejeniyar sulhu tsakaninsu wacce kuma ta tanadi kawo karshen aiwatar da ayyuka karkashin gwamnatoci biyu, kamar yadda suka rika yi a daa, wato Fatah na jagorantar gabar yamma da tekun jordan a yayinda ita kuma Hamas ke jagorantar zirin Gaza. Wannan rabuwan kai tsakanin kungiyoyin na daya daga cikin abubuwan da suka kawo tsaiko a yarjejeniyar sulhun yankin da Israila.

Mawallafiya: Pinado Abdu-Waba
Edita: Saleh Umar Saleh