1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan: Masu zanga-zanga sun gamu da fushin 'yan sanda

Abdoulaye Mamane Amadou
June 30, 2019

'Yan sandan Sudan sun amfani da hayaki mai sa kwalla kan tarin masu zanga-zanga da suka fito don zafafa matsin lamba ga gwamnatin mulkin soja da ta mika jan ragamar mulki a hannu farar hula.

https://p.dw.com/p/3LMLO
Sudan Khartum Massenproteste der Opposition
Hoto: AFP/E. Hamid

Shaidun gani da ido sun ce lamarin ya faru ne a wasu unguwanni na  Bari, al-Mamoura da Arkaweit, da ke wajen birnin Khartum inda dubban masu zanga-zangar da suka fito suka yi dandazo. Wasu rahotanni daga gabashin kasar ta Sudan musamman a Gadaref, sun ce a can din ma 'yan sanda sun harba hayaki mai sa hawaye kan masu zanga-zangar tare da tarwatsasu.
  
Jami'an tsaron kasar ta Sudan sun jibge askarawan rundunar RSF kan motoci da makamai a ko'ina cikin birnin a wani mataki na shirin ko ta kwana. Wannan al'amarin na zuwa ne duk da kiraye-kiranyen kwantar da tarzoma da kiyaye hakin masu zanga-zanga da hukumomin kare hakin dan Adam na kasa da kasa suka yiw a gwamnatin rikon kwarya ta kasar Sudan, duba da yadda aka samu kisan jama'a masu bore da adawa da gwamnatin mulkin soja a farkon wannan wata.