1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An bude rumfunan zabe a Turkiyya

May 14, 2023

Al'ummar kasar Turkiyya sun fita kada kuru'u a zaben shugaban kasa da ka iya tsawaita wa'adin mulkin shugaba Recep Tayyip Erdogan da ya shafe tsawon shekaru 20 ya na mulki.

https://p.dw.com/p/4RJqg
Hoto: Francisco Seco/AP Photo/picture alliance

Wannan dai zaben shi ne mafi kalubale ga Recep Tayyip Erdogan mai shekaru 69 ke fuskanta yayin da ake kallon zaben a matsayin mai mahimmanci.

Jagoran adawa, Kemal Kilicdaroglu da ke fatan kai gwamnatin Erdogan kasa dai, na da goyon bayan jam'iyyun adawa shida. A hannu guda kuma Erdogan ya sanya kafa ya shure rade-radin da ake na cewa, ba zai mika mulki ba in har bai yi nassara a zaben ba.

A kalla mutane miliyan 61 ne ake sa ran za su fito zaben ciki har da miliyan 5 da wannan ne karonsu na farko na kada kuru'a. Tuni dai Turkawa da ke kasashen ketare suka kada nasu kuru'un.