1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a Sudan ta Kudu

May 10, 2014

Bangarorin da ke rikici a kasar Sudan ta Kudu sun saka hannu kan yarjejeniyar tsagaita wuta domin kawo karshen rikicin da ke faruwa a kasar.

https://p.dw.com/p/1BxQl
Südsudan - Abkommen
Hoto: Reuters

Shugaban kasar Sudan ta Kudu Salva Kiir da madugun 'yan tawaye Riek Machar sun saka hannu kan yarjejeniyar tsagaita wuta, cikin wani matakin martani daga matsin lambar kasashen duniya.

A wannan Jumma'a da ta gabata aka amince da yarjejeniyar a birnin Addis Ababa na kasar Habasha. Wannan ya zama karo na farko da shugabannin suka fuskanci juna tun bayan barkewar rikici a watan Disamban 2013 kan gwagwarmayar samun madafun iko. Kiir da Machar sun amince da gwamnatin wucin gadi zuwa lokacin zaben shekara mai zuwa.

Bisa yarjejeniyar za a tsagaita wuta cikin sa'o'i 24.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Mohammad Nasiru Awal