1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An alkawarta wa Somaliya taimako mai yawa

May 7, 2013

A wannan Talata a birnin London wakilai daga kasashe sama da 50 da kuma kungiyoyin agaji daga ko'ina a duniya suka gudanar da taro a kan hanyoyin tallafa wa Somaliya.

https://p.dw.com/p/18TiZ
British Prime Minister David Cameron (L) looks on as Somali President Hassan Sheikh Mohamud (R) speaks during a press conference at the Foreign and Commonwealth Office in central London on May 7, 2013. British Prime Minister David Cameron warned that failure to support the rebuilding of Somalia will lead to 'terrorism and mass migration', as he opened an international meeting aimed at helping to end more than 20 years of conflict. Representatives of more than 50 countries and organisations were attending the London conference, which is co-hosted by Cameron and Somali President Hassan Sheikh Mohamud. AFP PHOTO/BEN STANSALL (Photo credit should read BEN STANSALL/AFP/Getty Images)
Hoto: AFP/Getty Images

Prayim Ministan Britaniya Mr. David Cameron da shugaba Hassan Sheikh Mohamud na Somaliya sune ke daukar bakoncin taron a birnin London. Lokacin jawabi ga masu neman labarai a bayan taron da ya samu wakilcin kasashe fiye da 50 da kuma kungiyoyin agaji, David Cameron, Prayim Ministan na Britaniya, matashiya yayi kan abin da yace wai ayyukan tarzoma da ta'addancin da ya zame babbar guba a zukatan matasan kasar Somalia.

"Wannan babbar barazana ce ga harkokinmu na tsaro, kuma idan muka yi ko burus da wannan barazana to kuwa za mu maimaita kura-kuran da muka yi a Afghanistan a shekarun dubu da dari tara da casa'in.

Taimakon sake gina Somaliya

Kan irin kuduri da alwashin da kasashe tajirai suka ci wa Somaliya alwashi kuma, tuni dai Birtaniya ta ci alwashin bai wa kasar dake a yankin kahon Afirka gudummawar fam miliyan goma, kwatankwacin Dolar Amurka miliyan goma sha biyar domin bunkasa harkokinta na tsaron kasa.

LONDON, UNITED KINGDOM - MAY 7: Prime Minister David Cameron (L) and Somali President Hassan Sheikh Mohamud (C) shake hands after making their opening speeches during the Somali conference, on May 7, 2013 in London, England. The international conference aims to help rebuild the east African country after more more than two decades of conflict. (Photo by Andrew Winning - WPA Pool/Getty Images)
Hoto: Getty Images

Haka kuma Mr. Cameron ya jaddada muhimmancin dake tare da bunkasa tattalin arzikin kasar ta Somalia, da kuma tabbatar da tafarkin demokradiyya a kasar.

Prayim Ministan na Britaniya ya zayyana irin nasarorin da suka cimma a Somaliya tun bayan taron farko da aka yi a bara.

Tabbatar da hadaddiyar kasar Somaliya

LONDON, UNITED KINGDOM - MAY 7: Kenya's President Uhuru Kenyatta (C) listens as Prime Minister David Cameron opens during the Somali conference, on May 7, 2013 in London, England. The international conference aims to help rebuild the east African country after more more than two decades of conflict. (Photo by Andrew Winning - WPA Pool/Getty Images)
Hoto: Getty Images

Shi kuwa a nasa jawabin, Shugaba HassanSheikh Mahmud na Somaliya, bayan godiya ga mahalarta taron, cewa yayi babban burin kasar Somaliya, shi ne ganin an tabbatar da hadaddiyar kasar Somaliya kuma zaune cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya mai dorewa.

"Wannan burin kwanciyar hankali kuwa muna fatan zai shafi fannin siyasa, tattalin arziki, da tsaro".

Shugaban na Somaliya ya tunasar da cewa hankalin duniya na zauren wannan taro to amma, al'ummar Somaliya wannan al'amari ya shafa. Shugaba Hassan Sheikh Mahmud, ya jaddada matsayinsa da gwamnatinsa a Somaliya cewa a shirye suke domin tabbatar da tafarkin demokradiyya da ya hada duka al'ummar Somaliya, karkashin tsarin da suka gabatarwa taron domin kawo sauyi a Somalia.

Mawallafi: Mohammed Sani Dauda
Edita: Mohammad Nasiru Awal