1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amurka ta ce Edmundo Gonzale ne shugaban Venezuela

Abdullahi Tanko Bala
August 2, 2024

Amurka ta ce akwai hujjoji da dama da suka nuna Edmundo Gonzalez Urrutia shi ne ya lashe zaben shugaban kasar Venezuela

https://p.dw.com/p/4j1gj
Venezuela I  Edmundo Gonzalez
Venezuela I Edmundo GonzalezHoto: Alfredo Lasry R/Getty Images

Amurka ta mince da dan takarar jami'ar adawa Edmundo Gonzalez Urrutia a matsayin wanda ya yi nasarar lashe zaben shugaban kasar Venezuela

Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken a cikin wata sanarwa ya ce bisa ga hujjoji kwarara da aka samu, a baiyane ta ke ga Amurka musamman jama'ar Venezuela cewa Edmundo Gonzalez Urrutia shi ne ya sami kuri'u mafi rinjaye a zaben shugaban kasar Venezuela na ranar 28 ga watan Yuli.

A ranar Litinin da ta gabata hukumar zaben Venezuela ta ayyana shugaba Nicolas Maduro a matsayin wanda ya lashe zaben, lamarin da ya haifar da zanga zanga a Caracas babban birnin kasar.

Yan adawa da gwamnatocin kasashen waje sun yi watsi da sakamakon da aka fitar a hukumance. Yayin da gwamnatin ta mayar da martani da kama daruruwan yan adawar. Kungiyar kare hakkin bil Adama ta Venezuela Foro Penal ta ce an kashe akalla mutane 11 a zanga zangar.