1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan zata fita cikin zargin Amirka

Abdul-raheem Hassan
July 5, 2018

Wani jami'ain diplomasiyyar kasar Amirka a Sudan ya yi alkawarin cire gwamnatin Khartoum cikin jerin kasashen da Amirka ke zargi da taimakawa kungiyoyin ta'adda.

https://p.dw.com/p/30rKL
NO FLASH Sudanesischer Präsident Al-Baschir
Hoto: picture alliance/dpa

Matakin na Amirka ya biyo bayan matakan mastin lamba da ta yi wa Sudan na katse hula da dangantakar soji da Koriya ta Arewa. Sudan na fuskantar wariyar huladar kasuwaci da sauran kasashen dunyia bisa takunkumin karan tsaana da Amirka ta likamata da ta'addanci.

A shekarar 1997  Amirka ta shigarda Sudan cikin jerin kasahsen da ke marawa 'yan ta'adda baya, lokacin da aka zargi shugaban Al-Qaeeda Usama bin Laden na samun mafaka a kasar tsakanin shekarun 1992 zuwa 1996.

A yanzu dai Sudan na fatan Amirka ta share sunanta cikin jerin kasashen duniya ke ganin suna bawa kungiyoyin tarzoma goyon baya, matakin da zai taimaka wajen farfado da tattalin arzikinta da durkushe shekara da shekaru.