1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka ta yaba wa jagoran yakin Libiya

April 20, 2019

Fadar White House ta Amirka ta tabbatar da zantawar Fadar White House ta Amirka ta tabbatar da zantawar Shugaba Donald Trump da madugun yakin Libiya Khalifa Haftar ta wayar tarho yayin da rikici ke kazanta.

https://p.dw.com/p/3H7zZ
USA, Washington: Donald Trump zieht Schnute
Hoto: Reuters/C. Barria

White House din ta ce tattaunawar wacce a cikinta Shugaba Trump ya yaba wa madugun yakin na Libiya, na daga cikin tsayuwar da Amirka na ganin an yaki ta'addanci da ma kare albarkatun man kasar.

To, sai dai masu kallon al'amura na fassara ganawar ta Juma'a, musamman yaba wa Haftar da Trump din ya yi, a matsayin taimaka masa ne a gwagwarmayar da yake yi don kwace iko a Libiyar.

Tattaunawar ta zo ne yayin kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ke fadi-tashin ganin an tsagaita wuta.