1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Alkalan Indiya sun soki babban jojin kasar

Zulaiha Abubakar
January 12, 2018

Alkalai hudu a kotun kolin kasar indiya sun yi hasashen cewar dimukaradiyya na fuskantar barazana saboda yadda ake gudanar da shari’u a kotuna ba tare da bin dokoki ba.

https://p.dw.com/p/2qmRs
Indien Gericht in Neu Delhi Anklage Gericht Demonstration
Hoto: dapd

Alkalan sun bayyana hakan ne a wani taron manema labarai irinsa na farko da suka kira inda su ka yi korafi kan babban Jojin kotun koli Dipak mishra cewar baya bin dokokin da aka shimfida a tsarin aikinsu, sannan yana yin yadda ya so da shari'un da aka gabatar masa. Ya zuwa yanzu dai babu wani martanin kare kai daga babban Jojin kotun kolin.

Daga bangaren Gwamnatin kasar kuwa wasu mataimakan Firayim ministan kasar Narendra Modi sun bayyana cewar yana nazarin al'amarin kuma a halin yanzu ya nemi ganawa da Manyan jami'an ma'aikatar Shari'ar kasar don nemo bakin zaren.