1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka ta Kudu

Afirka ta Kudu: Tankiya a kan rabon mukaman gwamnati

Abdourahamane Hassane
June 24, 2024

A Afirka ta Kudu har yanzu ba a fitar da wani bayani ba, a hukumance kan adadin mukaman da 'yan adawa za su samu a cikin gwamnatin hadaka da aka cimma yarjejeniya a makon jiya.

https://p.dw.com/p/4hRni
Hoto: Jerome Delay/AP/picture alliance

Sai dai a cikin 'yan kwanakin nan, jaridun kasar, sun ba da rahoton samun tashin hankali a tattaunawar da ake yi tsakanin jam'iyyar  ANC da babbar jam'iyyar adawa ta Democratic Alliance DA ta 'yan Liberal. A cewar wadannan bayyanai cikin kusan mukaman ministoci guda 30, Jamiyyar DA na bukatar samun goma yayin da ANC ta ce za ta iya ba su mukamai biyar ne kawai. A Afirka ta Kudun gaba daya jam'iyyun siyasa goma ne suka rattaba hannu kan yarjejeniyar kafa gwamnatin hadin kan kasa musamman ANC. da  DA da wasu  kananan jam'iyyu  siyasa.