1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taliban na kara karfin ikonta

Lateefa Mustapha Ja'afar
August 8, 2021

Rahotanni daga Afghanistan na nuni da cewa, mayakan Taliban sun kwace iko da baban birnin gundumar Kundus da ke arewacin kasar.

https://p.dw.com/p/3yj5T
Afghanistan Taloqan | Afghanische Milizen
Taliban na kara karfi da fadada ikonta a AfghanistanHoto: NASEER SADEQ/AFP/Getty Images

Wata sanarwa da majalisar dokokin gundumar ta Kundus ta fitar, ta nunar da cewa tuni 'yan Taliban din suka kwace iko da muhimman gine-ginen gwamnati, yayin da jami'an tsaro suka janye daga hanyar da ke zuwa filin jiragen sama na gundumar. Cikin 'yan kwanakin da suka gabata dai, Taliban din ta kwace iko da manyan biranen gundumomi uku. Tun bayan sanar da janyewar dakarun Amirka da na kungiyar tsaro ta NATO daga Afghansitan zuwa karshen wannan wata na Agusta da muke ciki, kungiyar Taliban ke kara fadada ikonta a yankuna da dama tare da kai munanan hare-hare.