1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ƙoƙarin shawo kan rikicin Libiya

June 16, 2011

Mahukunta a Libiya sun bayyana haƙoron cimma sulhu da 'yan tawaye muddin babu sharaɗin saukar Gadhafi daga mulki

https://p.dw.com/p/11cka
Mikhail Marglov, manzon Rasha na musamman akan lamuran Afirka yayin ziyara a Benghazi ranar 07.07. 2011.Hoto: dapd

Jakada na musamman da ƙasar Rasha ta tura zuwa ƙasar Libiya ya ce firaministan ƙasar ta Libiya ya bayyana masa cewar mahukunta a birnin Tripoli suna gudnar da tattaunawa tare da 'yan tawayen ƙasar dake da hedikwata a birnin Benghazi, tare da bayyana cewar ganawar tana gudana ne a can birnin Paris na ƙasar Faransa. Kamfanin dillancin labaran ƙasar Rasha ya ruwaito cewar gwamnatin shugaba Mouamer Gadhafi ta yi watsi da batun ya sauka daga muƙamin sa a lokacin wata tattaunawar da aka shirya a birnin na Tripoli a wannan Alhamis.

A halin da ake ciki kuma Ƙungiyar tarayyar Afirka ta gargaɗi Majalisar Ɗinkin Duniya cewar hare-haren soji a ƙasar Libiya, wani mummunan lamari ne dake wakana. Tuni dama taron ministocin ƙasashen Afirka ya buƙaci tsagaita buɗe-wuta domin bada damar warware matsalolin ta hanyar siyasa.

Jakadan Birtaniya a Majalisar Ɗinkin Duniya Mark Lyall Grant ya bayyana cewar, mai yiwuwa ba za'a tsagaita buɗe-wuta ba idan har shugaba Gadhafi bai yi murabus ba.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh

Edita : Ahmad Tijani Lawal