Turkiya na ci gaba da fafutikar zama mambar EU
March 26, 2018Talla
Erdogan ya bayyana haka ne gabannin tafiyarsa zuwa taron kolin kungiyar a Bulgeriya. Ya ce zai kuma tabo batun abin da ya kira gazawar kasashen na Turai wajen cika alkawuran da suka dauka a dangane da 'yan gudun hijirar Siriya. Taron kolin dai za a yi ne a gabar tekun Varna gefen Bahar Asuwad.
Turkiya dai na ci gaba da matsa lamba wajen ganin an cusata cikin kungiyar kasashen na Turai duk da irin turjiya da take fiskanta a tattaunawar da ake da ita kan batun.