Tattauna rikicin Libiya a Berlin.
June 10, 2015Talla
Majalissar Ɗinkin Duniya ta buɗe wani zaman taron kan batun ƙasar Libiya a birnin Berlin.Taron wanda ya samu halartar wakillan ƙasar Libiya 23 da kuma na wasu manyan ƙasashen duniya, na da ɓurin ɗaukar matakan samar da zaman lafiya a ƙasar Libiya da zumar hana mata wargajewa a cewar ministan harakokin wajen ƙasar Jamus Frank-Walter Steinmeier a cikin wata sanarwa da ya gabatar a zauran taron.
Taron na Birnin Berlin na kuma da ɓurin ganin bangarorin da ke hamayya da juna a ƙasar ta Libiya sun amince ga saka hannu a kan wata yarjejeniyar kafa gwamnatin haɗa kan kasa da aka cimma a taron da ya wakana a ƙasar Maroko kan batun ƙasar ta Libiya.