A cikin shirin za a ji cewar shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya yi wata tattaunawa da manyan jami'an gwamnatinsa domin kawo karshen zanga zanga mafi muni da kasar ta fuskanta cikin shekaru hamsin da suka gabata. A Jamhuriyar Nijar kuwa Jam’iyyar matasa ta CPR INGANCI ta fada rikicin cikin gida da ya janyo wani bangare yace ya dakatar da shugaban jam’iyya.