Libiya ta buƙaci agajin Majalisar Ɗinkin Duniya
August 13, 2014Talla
Majalisar ta kaɗa ƙuri'ar amincewa da wani daftarin ƙudiri wanda ke ba da izinin kwance ɗamarar dakarun sa kai na ƙasar.
Wannan doka ta shafi ƙungiyoyin mayaƙan sa kai waɗanda ke da alaƙa da 'yan aware na garin Misirata. Sai dai wani abin da ba a a tabbas a kansa shi ne cewar ko majalisar na da ƙarfin ikon zartas da wannan doka ga gwamnatin da har yanzu ba ta da cikakken iko wajen tafiyar da harkokin tsaro a ƙasar.
Mawallafi: Abdourahamane Hassane
Edita : Suleiman Babayo