An kiyasta cewa kashi daya bisa uku na yaran makiyaya a Lesotho ba sa zuwa makaranta. Suna shafe tsawon yini wajen nema wa dabbobi abin da za su ci. Sai dai wani tsohon makiyayi mai suna Julius Mojoro ya kafa makarantar dare domin ya tabbatar da cewa sun iya karatu da rubutu.