Falasɗinu za ta kafa tutarta a Majalisar Ɗinikin Duniya
September 10, 2015Talla
Majalisar Ɗinkin Duniya za ta bai wa Falasɗinu izinin kafa tutarta a cibiyar majalisar da ke a New York,a wani sabon mataki na fafutukar diplomasiyya da za ta kai ga amincewar majalisar da ƙasar a matsayin ƙasa mai cikakken yanci.
Nan gaba zuwa da yamma majalisar za ta gabatar da wani ƙudurin na musammun a kan lamarin a taron da za ta yi, wanda kuma bisa ga dukkan alamu ake ganin na cikka suna ne kawai.ko da shi ke ma kawo yanzu ana nuna rashin tabbas a kan matsayin ƙasashen Ƙungiyar Tarrayar Turai masu ra'ayoyi mabanbanta. Amirka da da Isra'ila na yin adawa da wannan ƙudiri kamar yadda suka yi a lokacin da Falasɗinu ta samu matsayin yar kallo a majalisar a shekarun 2012.