1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana ci gaba da samun tashin hankali a Libiya

October 22, 2012

Masu zanga zanga sun nemi kawo karshen rikicin da ke faruwa a garin Bani Walid na Libiya.

https://p.dw.com/p/16UDj
Hoto: picture alliance/dpa

Masu zanga zanga sun kutsa majalisar dokokin ƙasar Libiya, a wannan Lahadin da ta gabata, inda su ke neman ganin ɗaukan matakan shawo kan rikicin garin Bani Walid, inda ake ɗauka tungar hamɓararren Shugaba Marigayi Mu'ammar Gaddafi.

Masu ɗauke da makamai daga Misrata da ke da alaƙa da ma'aikatan tsaro, sun kai harin birnin mai jama'a 70,000, da ya hallaka mutane 22, tare da jikata fiye da mutane 200.

Sabbin mahukuntan ƙasar ta Libiya sun gudanar da zaɓe, amma har kawo yanzu babu cikekken doka da oda, shekara guda bayan kawar da gwamnatin Marigayi Gaddafi ta Shekaru 42.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Halima Balaraba Abbas