SiyasaAfirka
Mahara sun kai wa masallaci a hari a Tillabery
August 21, 2021Talla
Gwamnan jihar Tillabery Ibrahim Tidjani ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Jamus, DPA, cewa maharan kan babura dauke da muggan makamai sun afka cikin masallacin kauyen Anzarou a yayin da mazauna ke tsaka da ibada, inda suka halaka mutane.
Harin na kauyen Anzarou da ke kan iyakar Nijar da Mali na zuwa ne 'yan kwanaki bayan da mahara suka kashe mutane 37 ciki har da kananan yara a yankin na Tillabery da ke yammacin Jamhuriyar Nijar.