1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Al'ummar Libiya ta ƙaddamar da zaɓe

July 7, 2012

Bayan sama da shekaru 40 a ƙarƙashin mulkin kama karya, al'ummar Libiya ta fito cikin ɗoki da walwala dan gudanar da zaɓen 'yan majalisar da zata share fagen gudanar da mulki bisa tanadin shika-shikan demokraadiyya

https://p.dw.com/p/15TII
Women queue to cast their ballot during the National Assembly election at a polling station in Tripoli July 7, 2012. Libyans, some with tears of joy in their eyes, queued to vote in their first free national election in 60 years on Saturday, a poll designed to shake off the legacy of Muammar Gaddafi but which risks being hijacked by violence. REUTERS/Zohra Bensemra (LIBYA - Tags: POLITICS ELECTIONS)
Mata ma ba'a barsu a baya baHoto: Reuters

An buɗe runfunan zaɓe a Libiya domin gudanar da abun da ake sa ran zai zama zaɓe mafi sahihanci a ƙasar bayan shekaru 60.

Wato shekaru 40 na mulkin kama karyar marigayi Kanar Mu'ammar Gaddafi.

Waɗanda suka cancanci jefa ƙuri'ar masu yawan aƙalla milliyan uku, zasu zaɓi majalisa ce mai mambobi 200 wacce kuma zata zaɓi Frime Minista da Majalisar Ministoci, kafin daga bisani ta yi shinfidar gudanar da zaɓen 'yan Majalisar dokoki wanda ake kyautata zaton gudanarwa a badi idan Allah ya kaimu, bisa tanadin sabon kundin tsarin mulkin ƙasar, wanda shima Majalisar zata ɗauki nauyin girkawa.

Abubakar Halloul wani ma'aikacin gidan rediyo ne a Libiyan wanda ke ɗokin gudanar da aikin jaridarsa cikin walwala a lokacin wannan zaɓe.

"Wannan ne karon farko da muke da damar yin aikinmu cikin walwala, zamu iya amfani da shiƙa-shiƙan demokradiyya ba tare da mun ɓoye wasu batutuwa ba, yanzu ma zan iya zantawa da jama'a a kan hanya, in basu damar bayyana ra'ayoyinsu in kuma sanya a rediyo yadda kowa da kowa zai ji ya kuma amfana"

Mawallafiya: Pinaɗo Abdu Waba
Edita: Zainab Mohammed Abubakar